Abdoulaye Ousmane | |||||||||||||||||||
---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|
Rayuwa | |||||||||||||||||||
Haihuwa | Maubeuge (en) , 22 ga Faburairu, 2000 (24 shekaru) | ||||||||||||||||||
ƙasa | Muritaniya | ||||||||||||||||||
Sana'a | |||||||||||||||||||
Sana'a | ɗan wasan ƙwallon ƙafa | ||||||||||||||||||
|
Abdoulaye Ousmane (Larabci: عبد الله عثمان; an haife shi a ranar 22 ga watan Fabrairu 2000) ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne wanda ke taka leda a matsayin mai tsaron baya a ƙungiyar Lille Reserve ta Faransa. An haife shi a Faransa, yana wakiltar Mauritania a matakin kasa da kasa.[1]
Ousmane ya fara wasansa na farko na ƙwararru da kungiyar kwallon kafa ta Strasbourg a cikin rashin nasara da ci 2–0 a Coupe de France a hannun Montpellier a ranar 10 ga watan Fabrairu 2021.[2]
A farkon watan Fabrairu 2022, Ousmane ya koma kulob din Girka Apollon Larissa kan kwantiragin har zuwa Yuni 2023. [3] Duk da haka, ya bar kulob din a watan Yuli.
Daga nan Ousmane ya koma kungiyar Lille ta Faransa a ranar 22 ga watan Satumba 2022. [4]
An haife shi a Faransa, Ousmane dan asalin Mauritaniya ne. Ya buga wasansa na farko a tawagar kasar Mauritania a ranar 26 ga watan Maris 2021 a wasan neman tikitin shiga gasar AFCON 2021 da Morocco.[5]