Datti Abubakar | |||
---|---|---|---|
ga Yuli, 1978 - Oktoba 1979 ← John Kpera - Jim Ifeanyichukwu Nwobodo → | |||
Rayuwa | |||
Cikakken suna | Datti Sadiq Abubakar | ||
Haihuwa | jahar Kano, 30 ga Maris, 1939 | ||
ƙasa | Najeriya | ||
Ƙabila | Hausawa | ||
Harshen uwa | Hausa | ||
Mutuwa | 25 ga Faburairu, 2005 | ||
Karatu | |||
Harsuna |
Turanci Hausa Pidgin na Najeriya | ||
Sana'a | |||
Sana'a | ɗan siyasa |
Datti Sadiq Abubakar ya kasance gwamnan soja na jihar Anambra a Najeriya daga Yuli 1978 zuwa Oktoba 1979 a lokacin mulkin soja na Janar Olusegun Obasanjo.[1]
Ya yi karatu a Kwalejin Rumfa, Kano.[2] A watan Yulin shekarar 1966 Laftanar Datti Abubakar, mai suna Recce, ya kasance a kurkukun Abeokuta lokacin da aka kashe yawancin jami'an Igbo, sun taka rawar gani a juyin mulkin da suka hambarar da Manjo-Janar Johnson Aguiyi-Ironsi.[3]
An naɗa Abubakar gwamnan soja na jihar Anambra a watan Yulin 1978, ya rike wannan mukamin har zuwa watan Oktoba 1979.[1] Ya sanya makarantun a ƙarƙashin ikonsa ta hanyar kwamiti na dubawa tare da manyan iko akan manufofi da ma'aikata.[4] Bayan manyan rikice-rikice na addinai a jihar Kano a 1980, ya kasance memba a Kotun Binciken Rukunin Kano don bincika dalilai da bayar da shawarwari. kum ya kasance musulmi mazauin garin Kano.[5]