Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta ƙasar Najeriya | |
---|---|
Hukumar kare hakkin ɗan Adam |
Hukumar kare Haƙƙin ɗan Adam ta ƙasa ( NHRC ), an kafa hukumar kare hakkin dan adam ta kasa (NHRC), a shekara ta alif dari tara da casa'in da biyar 1995, kamar yadda dokar (NHRC), ta shekara ta dubu biyu da goma 2010, ta gyara. Hukumar tana aiki ne a matsayin wata hanya ta wuce gona da iri wacce ke kare hakkin bil'adama na al'ummar Najeriya. Tana sa ido a kan hakkin dan Adam a Najeriya, tana taimakawa wadanda aka take haƙƙin su, da kuma taimakawa wajen tsara manufofin gwamnatin Najeriya kan hakkin dan adam. [1]
Hukumar ta kasance mai himma wajen bincike da lura da al'amuran kare haƙƙin bil'adama da damar kafuwarta. [2][3] Amnesty International ta nuna damuwa game da tsoratar da Hukumar Kare Haƙƙoƙin Ɗan Adam ta ƙasa da rundunar 'yan sandan Najeriya ke yi a shekara ta dubu biyu da goma sha biyu 2012.[4]
Sakataren zartarwa na yanzu shine Anthony O. Ojukwu Esq.