Kader Mangane | |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|
Rayuwa | |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Haihuwa | Thiès (en) , 23 ga Maris, 1983 (41 shekaru) | ||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
ƙasa |
Faransa Senegal | ||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Karatu | |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Harsuna | Faransanci | ||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Sana'a | |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Sana'a | ɗan wasan ƙwallon ƙafa | ||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
| |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Mahalarcin
| |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Muƙami ko ƙwarewa | centre-back (en) | ||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Lamban wasa | 15 | ||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Tsayi | 193 cm |
Abdou Kader Mangane (an haife shi ranar 23 ga watan Maris ɗin shekara ta 1983) tsohon ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne kuma ɗan ƙasar Senegal wanda ya taka leda a matsayin mai tsaron gida. Ya shafe yawancin aikinsa a Faransa. A matakin ƙasa da ƙasa, ya buga wa tawagar ƙasar Senegal wasanni 23 inda ya ci ƙwallo 1.
Mangane ya fara aikinsa a ƙasarsa ta Senegal kafin ya koma Switzerland da Neuchâtel Xamax a cikin shekarar, 2001, inda kuma ya shafe shekaru shida. Sannan ya tafi buga wasanni biyar a Ligue 1 na Faransa, don Lens[1] a lokacin kakar shekara ta, 2007 zuwa 2008, da Rennes.[2]
A ranar 17 ga watan Yulin shekara ta, 2012, Mangane ya rattaɓa hannu kan kwangilar shekaru uku tare da kulob ɗin Al-Hilal na Saudiyya kan kuɗin da ba a bayyana ba.[3]
Ya koma ƙungiyar Sunderland ta Premier League a matsayin aro har zuwa ƙarshen kakar wasa a ranar 14 ga watan Janairun shekara ta, 2013.[4]
A ranar 31 ga watan Yulin shekara ta, 2015, Mangane ya rattaɓa hannu kan Gazélec Ajaccio akan kwangilar shekara guda.[5]
A ranar 21 ga watan Maris a shekara ta, 2009, yayin wasan Ligue 1 da Valenciennes ya yi wa ɗan wasan gaba Jonathan Lacourt rauni sosai a wani ƙalubale wanda ya haifar da karaya biyu na tibia da fibula. An dakatar da shi har zuwa ranar 1 ga watan Yunin shekara ta, 2009.[6]
Mangane ya sami takardar zama ɗan ƙasar Faransa a ranar 16 ga watan Mayun shekara ta, 2011.[7]