![]() | |
---|---|
writers’ organization (en) ![]() | |
Bayanai | |
Farawa | 1981 |
Shafin yanar gizo | ananigeria.org |
Ƙungiyar Marubuta ta Najeriya ( ANA ) ƙungiya ce mai zaman kanta wacce ke haɓaka adabin Najeriya . Tana wakiltar marubutan Najeriya masu kirkire-kirkire a gida da waje. Marubuci dan Najeriya Chinua Achebe ne ya kafa ta a shekarar 1981 a matsayin shugabanta. [1] [2] Tsohon shugaban na kusa shine Alhaji Denja Abdullahi. Shugaba mai ci shine Camilus Ukah sai kuma mataimakiyar shugaban Hajiya Farida Mohammed . [3]
An kafa kungiyar ne a ranar 27 ga watan Yunin 1981 shekaru goma bayan yakin basasar Najeriya, a wani taro a jami'ar Najeriya dake Nsukka . Taron ya samu halartar marubutan Kenya guda biyu, Ngũgĩ wa Thiong'o da Gacheche Wauringi. Bayan haka, Hukumar Kula da Harkokin Kasuwanci ta Najeriya ta yi rajistar kungiyar kamar yadda doka ta yanzu ta 1990 Vide Companies and Allied Matters Act No 1.
Wadanda suka kafa ANA sun hada da Kole Omotoso, Mabel Segun, Ernest Emenyonu, Labo Yari, Femi Osofisan, JP Clark, Niyi Osundare, Jerry Agada da TM Aluko . [4] [5]