Umar Bologi II | |
---|---|
Rayuwa | |
Haihuwa | 1980 (44/45 shekaru) |
Sana'a |
Umar Bologi (an haife shi a ranar 8 ga watan Fabrairu shekarar 1982) shi ne sarki na 7 Etsu Pategi, sarkin gargajiya na Masarautar Pategi, ya gaji marigayi Etsu Alhaji Ibrahim Umaru Chatta kuma Gwamna Abdulfatah Ahmed ya naɗa shi etsu a watan Afrilu, shekarar 2019.[1][2][3]
An haife shi a gidan sarauta na Masarautar Pategi. Ya yi digirin farko (B.Sc.). Ya karanci Public Administration a Jami’ar Abuja inda ya kammala a shekarar 2005 sannan a shekarar 2006 ya sami Diploma a fannin (Computer Hardware and Networking). Ya shiga Hukumar Kwastam ta Najeriya ne a shekarar 2010 bayan ya kammala karatunsa na farko na Course, a matsayin jami’in gudanarwa, ya riƙe muƙamin jami’in hulda da jama’a na Jihar Kwara da kuma Kaduna a shekarar 2011, ya kuma kasance jami’in sadarwa, Kamfanin Pipeline & Product Marketing, Kaduna a 2007 da kuma bayanai. Jami’in kula da kula da harkokin suga na ƙasa a Abuja 2013, a matsayin mataimakin Sufeto ya kasance mai aiki na I a shekarar 2019 wanda shi ne muƙamin karshe da aka yi a hukumar kwastam, kafin daga bisani a ranar 16 ga watan Afrilu shekarar 2019 aka naɗa shi a matsayin sarkin gargajiya na Etsu Patigi na masarautar Pategi. Kuma a matsayin babban shugaba na farko.[4][5]