![]() | |
---|---|
Rayuwa | |
Haihuwa | Bamako, Nuwamba, 1956 (68 shekaru) |
ƙasa | Mali |
Karatu | |
Makaranta |
Université Cheikh Anta Diop (en) ![]() Toulouse Capitole University (en) ![]() |
Harsuna | Faransanci |
Sana'a | |
Sana'a | ɗan siyasa |
Sidibé Aminata Diallo, (an haife ta a shekara ta 1950) mai ilimi ce kuma ƴar siyasa ce sannan ƴar ƙasar Mali ce .[1] Sidibe Aminata Diallo farfesa ce a fannin tsara gari a Jami'ar Bamako kuma ta taɓa yi wa UNESCO aiki.[2]
Diallo ta sami digiri na uku a fannin haɓakawa da karatun birni daga Jami'ar Toulouse a shekarar 1984. Ita kuma mamba ce a tsangayar Kimiyyar Tattalin Arziki da Gudanarwa a Jami'ar Bamako, inda ta ƙware a fannin sarrafa filaye. [3]
A ranar 12 ga watan Maris din shekarar 2007, Diallo ta ayyana matsayinta na tsayawa takarar shugaban ƙasa . [4] Ta kasance ɗaya daga cikin ƴan takara 8 da suka fafata a zaɓen shugaban ƙasa na watan Afrilun 2007 . Har ila yau, ita ce mace ta farko da ta kasance ƴar takarar shugaban ƙasa a Mali, kuma ta kasance 'yar takarar ' Movement for Environmental Education and Sustainable Development '. Babbar sha'awarta shi ne ɗorewa da kare muhalli. [3] Diallo ta samu ƙuri'u sama da 12,000 a zaɓen, kashi 0.55% na yawan kuri'u. [5]
Bayan zaɓen, an naɗa Diallo a matsayin Ministan Ilimi ta Farko, Karatu, da Harsuna na Ƙasa a ranar 3 ga watan Oktoban 2007. [6] Ta riƙe wannan muƙamin har sai da Salikou Sanogo ya maye gurbinsa a ranar 9 ga watan Afrilun 2009. [7]